Aliyu Zubairu Kauru
Director Strategy and Communications
An haifi Aliyu Zubairu a garin Kauru da ke Ƙaramar Hukumar Kauru ta jihar Kaduna, a ranar 20 ga watan Agustan 1995.
Ya halarci Model Primary School Kauru daga 2000 zuwa 2006, sannan ya wuce Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Kauru, inda ya kammala a 2013.
Ya samu shaidar kammala Diploma (ND) da (HND) a fannin aikin Jarida, 2014 zuwa 2019 a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli, Zariya.
Haka nan, ya yi wa Kasa Hidima (NYSC), a Jihar Ekiti a shekarar 2021.
Ya fara Aikin Jarida a shekarar 2016 da Gidan Talabijin da Rediyon Jihar Kaduna (KSMC) ƙarƙashin Sashen Labarai da Al’amuran Yau da Kullum a matsayin ma’aikacin sa-kai, daga baya kuma a shekarar 2018 ya samu aiki a matsayin ma’aikaci na dindindin.
A cikin wannan lokaci, ya samu shaidar jajircewar aiki daban-daban daga Hukumar Gudanarwar Kafafen Yaɗa Labarai ta Jihar Kaduna bisa ƙwazonsa da sanin makamar aiki.
Bugu da ƙari, ya halarci kwasai-kwasai da taron ƙara wa juna sani da dama, inda ya samu kyautukar karramawa.
📱08102863264
✉️ alyzub4u@gmail.com