Suraj Idris Sai’d

Staff

Suraj Idris Sai’d
Staff

An haife shi a ranar 10 ga watan Oktoba, na shekarar 1990, a garin Kududdufawa da ke Jihar Kano, Nijeriya.

Ya fara karatun Firamare a garin Katsinawa sannan ya koma Jajira Firamare, inda ya kammala a shekarar 2005. Ya wuce Makarantar Sakandare ta Jajira daga 2005 zuwa 2011.

Ya yi Difiloma a Jami’ar Bayero da ke Kano daga 2011 zuwa 2013 a fannin Jarida. Sannan ya fara Digiri a 2014, ya kammala a 2017 a Jami’ar ta Bayero da ke Kano, duk a fannin Jarida.

Bugu da ƙari, ya fara karatun Digiri na biyu a National Open University, inda ya kammala daga 2022 zuwa 2024, a fannin Jarida.

Ya kuma samu shaidar Difiloma a fannin Kwamfuta, sannan ya samu takardar horon aiki daga gidan Rediyon Muryar Amurka (VOA) a shekarar 2015.

Haka zalika, a fannin ilimin addini ya yi saukar Al-kur’ani tun a shekarar 2010 da sauran wasu littatafai na addini da dama.

A ɓangaren ayyuka, ya yi aiki da kafafen yaɗa labarai da dama, kamar haka; BUK Radio, da, Aminci Rediyo, da Arewa Rediyo, da Sawaba FM, da Arewa 24, da Labarai 24, da Amsal News, da Dimokuraɗiyya, da Kogin Wasanni, da kuma Mairiga’s Talk Show, dss.

Yanzu haka, shi ne Jami’in Yaɗa Labarai na kamfanin sarrafa Ƙarafa na Afuwa Welding Works and General Metal Construction. Sannan ƴa na aiki da gidan Rediyo da Talabijin na Muhasa, Kano.

📱 +2347038471566
✉️ surajnaiya0@gmail.com