Nana Asma’u Lawal Liman

Director Operations and Evaluation

Nana Asma’u Lawal Liman
Director Operations and Evaluation

Wacce aka haifa a ranar 26 ga watan Agusta na shekarar 2002, a Ƙaramar Hukumar Ƙaura-Namoda da ke jihar Zamfara a Tarayyar Najeriya.

Ta yi karatun Firamare a Nelson Mandela International School da ke garin Abuja, yayin da ta tafi Jihar Katsina inda ta yi Sakandare a makarantar Ulul-Albab Science Secondary School.

Har wa yau, ta kuma mallaki shaidar kammala karatun Diploma (ND) a fannin Ƙere-Ƙere (Civil Engineering Technology), a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya, Ƙaura-Namoda, Zamfara.

A ɓangaren karatun addini kuwa; Ta sauke Alkur’ani mai girma a 2019, ta kuma sake sauke wa a karo na biyu a shekara ta 2021.

Ta yi aiki da wasu Jaridun yanar gizo irinsu; One News Hausa, da Bakandamiya Reading Club.

Bugu da ƙari, Nana Asma’u (Queen-Nasmah), ta kasance shahararriyar marubuciya wacce ta yi shura a Duniyar Adabi. Yanzu haka, ita ce Shugabar ƙungiyar Moonlight Writers Association.

✉️ Asmaunanalawalliman@gmail.com